caseriqBinciken ma'ana a cikin Alqur'ani

Suratu As-Saaffaat الصافات

Ayoyi 182 · Makka · tsarin saukarwa 56

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ وَٱلصَّٰٓفَّٰتِ صَفًّا

Hausa Translation - Abu Bakr JumiInã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَٱلزَّٰجِرَٰتِ زَجْرًا

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSa'an nan mãsu yin tsãwa[1] dõmin gargaɗi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَٱلتَّٰلِيَٰتِ ذِكْرًا

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّ إِلَٰهَكُمْ لَوَٰحِدٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

رَّبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ ٱلْمَشَٰرِقِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiUbangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّا زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنْيَا بِزِينَةٍ ٱلْكَوَاكِبِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَحِفْظًا مِّن كُلِّ شَيْطَٰنٍ مَّارِدٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى ٱلْمَلَإِ ٱلْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiBã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

دُحُورًا وَلَهُمْ عَذَابٌ وَاصِبٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiDõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِلَّا مَنْ خَطِفَ ٱلْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُۥ شِهَابٌ ثَاقِبٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiFãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَٱسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَآ إِنَّا خَلَقْنَٰهُم مِّن طِينٍ لَّازِبٍۭ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKa tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiÃ'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِذَا ذُكِّرُوا۟ لَا يَذْكُرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِذَا رَأَوْا۟ ءَايَةً يَسْتَسْخِرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiIdan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَقَالُوٓا۟ إِنْ هَٰذَآ إِلَّا سِحْرٌ مُّبِينٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَءِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَبْعُوثُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَوَءَابَآؤُنَا ٱلْأَوَّلُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَٰخِرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKa ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌ وَٰحِدَةٌ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَقَالُوا۟ يَٰوَيْلَنَا هَٰذَا يَوْمُ ٱلدِّينِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

هَٰذَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiWannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

ٱحْشُرُوا۟ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ وَأَزْوَٰجَهُمْ وَمَا كَانُوا۟ يَعْبُدُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKu tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

مِن دُونِ ٱللَّهِ فَٱهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلْجَحِيمِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiWanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَقِفُوهُمْ إِنَّهُم مَّسْـُٔولُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

مَا لَكُمْ لَا تَنَاصَرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiMe ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

بَلْ هُمُ ٱلْيَوْمَ مُسْتَسْلِمُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiÃ'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَآءَلُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

قَالُوٓا۟ إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ ٱلْيَمِينِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSuka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

قَالُوا۟ بَل لَّمْ تَكُونُوا۟ مُؤْمِنِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSuka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَٰنٍۭ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًا طَٰغِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَآ إِنَّا لَذَآئِقُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَأَغْوَيْنَٰكُمْ إِنَّا كُنَّا غَٰوِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍ فِى ٱلْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِٱلْمُجْرِمِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّهُمْ كَانُوٓا۟ إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا ٱللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُوٓا۟ ءَالِهَتِنَا لِشَاعِرٍ مَّجْنُونٍۭ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

بَلْ جَآءَ بِٱلْحَقِّ وَصَدَّقَ ٱلْمُرْسَلِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiÃ'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّكُمْ لَذَآئِقُوا۟ ٱلْعَذَابِ ٱلْأَلِيمِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiFãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أُو۟لَٰٓئِكَ لَهُمْ رِزْقٌ مَّعْلُومٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiWaɗannan sunã da abinci sananne.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَوَٰكِهُ وَهُم مُّكْرَمُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiYa'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فِى جَنَّٰتِ ٱلنَّعِيمِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiA cikin gidãjen Aljannar ni'ima.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

عَلَىٰ سُرُرٍ مُّتَقَٰبِلِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiA kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍۭ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiAnã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

بَيْضَآءَ لَذَّةٍ لِّلشَّٰرِبِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiFarã mai dãɗi ga mashãyan.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

لَا فِيهَا غَوْلٌ وَلَا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiA cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَعِندَهُمْ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرْفِ عِينٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

كَأَنَّهُنَّ بَيْضٌ مَّكْنُونٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَآءَلُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

قَالَ قَآئِلٌ مِّنْهُمْ إِنِّى كَانَ لِى قَرِينٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiWani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

يَقُولُ أَءِنَّكَ لَمِنَ ٱلْمُصَدِّقِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiYanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَءِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَدِينُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

قَالَ هَلْ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَٱطَّلَعَ فَرَءَاهُ فِى سَوَآءِ ٱلْجَحِيمِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

قَالَ تَٱللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرْدِينِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiYa ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَوْلَا نِعْمَةُ رَبِّى لَكُنتُ مِنَ ٱلْمُحْضَرِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَفَمَا نَحْنُ بِمَيِّتِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِلَّا مَوْتَتَنَا ٱلْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ ٱلْفَوْزُ ٱلْعَظِيمُ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

لِمِثْلِ هَٰذَا فَلْيَعْمَلِ ٱلْعَٰمِلُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَذَٰلِكَ خَيْرٌ نُّزُلًا أَمْ شَجَرَةُ ٱلزَّقُّومِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiShin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّا جَعَلْنَٰهَا فِتْنَةً لِّلظَّٰلِمِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّهَا شَجَرَةٌ تَخْرُجُ فِىٓ أَصْلِ ٱلْجَحِيمِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

طَلْعُهَا كَأَنَّهُۥ رُءُوسُ ٱلشَّيَٰطِينِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiGundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَإِنَّهُمْ لَـَٔاكِلُونَ مِنْهَا فَمَالِـُٔونَ مِنْهَا ٱلْبُطُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

ثُمَّ إِنَّ لَهُمْ عَلَيْهَا لَشَوْبًا مِّنْ حَمِيمٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

ثُمَّ إِنَّ مَرْجِعَهُمْ لَإِلَى ٱلْجَحِيمِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّهُمْ أَلْفَوْا۟ ءَابَآءَهُمْ ضَآلِّينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَهُمْ عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِمْ يُهْرَعُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ ضَلَّ قَبْلَهُمْ أَكْثَرُ ٱلْأَوَّلِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَٱنظُرْ كَيْفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلْمُنذَرِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiFãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ نَادَىٰنَا نُوحٌ فَلَنِعْمَ ٱلْمُجِيبُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَنَجَّيْنَٰهُ وَأَهْلَهُۥ مِنَ ٱلْكَرْبِ ٱلْعَظِيمِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَجَعَلْنَا ذُرِّيَّتَهُۥ هُمُ ٱلْبَاقِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiMuka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

سَلَٰمٌ عَلَىٰ نُوحٍ فِى ٱلْعَٰلَمِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiAminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle shi, yanã daga bãyin Mu mũminai.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

ثُمَّ أَغْرَقْنَا ٱلْـَٔاخَرِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِۦ لَإِبْرَٰهِيمَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِذْ جَآءَ رَبَّهُۥ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiA lõkacin da ya je wa ubangijinsa da zũciya kuɓutacciya.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِۦ مَاذَا تَعْبُدُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiA lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَئِفْكًا ءَالِهَةً دُونَ ٱللَّهِ تُرِيدُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَنَظَرَ نَظْرَةً فِى ٱلنُّجُومِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَقَالَ إِنِّى سَقِيمٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَتَوَلَّوْا۟ عَنْهُ مُدْبِرِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَرَاغَ إِلَىٰٓ ءَالِهَتِهِمْ فَقَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

مَا لَكُمْ لَا تَنطِقُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Me ya sãme ku, bã ku magana?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَرَاغَ عَلَيْهِمْ ضَرْبًۢا بِٱلْيَمِينِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَأَقْبَلُوٓا۟ إِلَيْهِ يَزِفُّونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

قَالَ أَتَعْبُدُونَ مَا تَنْحِتُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiYa ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَٱللَّهُ خَلَقَكُمْ وَمَا تَعْمَلُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

قَالُوا۟ ٱبْنُوا۟ لَهُۥ بُنْيَٰنًا فَأَلْقُوهُ فِى ٱلْجَحِيمِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSuka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَأَرَادُوا۟ بِهِۦ كَيْدًا فَجَعَلْنَٰهُمُ ٱلْأَسْفَلِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَقَالَ إِنِّى ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّى سَيَهْدِينِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

رَبِّ هَبْ لِى مِنَ ٱلصَّٰلِحِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَبَشَّرْنَٰهُ بِغُلَٰمٍ حَلِيمٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai Muka yi masa bushãra da wani yãro [1]mai haƙuri.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ ٱلسَّعْىَ قَالَ يَٰبُنَىَّ إِنِّىٓ أَرَىٰ فِى ٱلْمَنَامِ أَنِّىٓ أَذْبَحُكَ فَٱنظُرْ مَاذَا تَرَىٰ قَالَ يَٰٓأَبَتِ ٱفْعَلْ مَا تُؤْمَرُ سَتَجِدُنِىٓ إِن شَآءَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلصَّٰبِرِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَلَمَّآ أَسْلَمَا وَتَلَّهُۥ لِلْجَبِينِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiYayin da suka mika wuya sai muka fansheshi da Rago

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَنَٰدَيْنَٰهُ أَن يَٰٓإِبْرَٰهِيمُ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

قَدْ صَدَّقْتَ ٱلرُّءْيَآ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ ٱلْبَلَٰٓؤُا۟ ٱلْمُبِينُ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَفَدَيْنَٰهُ بِذِبْحٍ عَظِيمٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِبْرَٰهِيمَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiAminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَبَشَّرْنَٰهُ بِإِسْحَٰقَ نَبِيًّا مِّنَ ٱلصَّٰلِحِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka yi masa bushãra[1] Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَبَٰرَكْنَا عَلَيْهِ وَعَلَىٰٓ إِسْحَٰقَ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحْسِنٌ وَظَالِمٌ لِّنَفْسِهِۦ مُبِينٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَنَجَّيْنَٰهُمَا وَقَوْمَهُمَا مِنَ ٱلْكَرْبِ ٱلْعَظِيمِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَنَصَرْنَٰهُمْ فَكَانُوا۟ هُمُ ٱلْغَٰلِبِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَءَاتَيْنَٰهُمَا ٱلْكِتَٰبَ ٱلْمُسْتَبِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَهَدَيْنَٰهُمَا ٱلصِّرَٰطَ ٱلْمُسْتَقِيمَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَتَرَكْنَا عَلَيْهِمَا فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

سَلَٰمٌ عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiAminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّهُمَا مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle, sunã daga bãyin Mu mũminai.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِنَّ إِلْيَاسَ لَمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِذْ قَالَ لِقَوْمِهِۦٓ أَلَا تَتَّقُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiA lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَتَدْعُونَ بَعْلًا وَتَذَرُونَ أَحْسَنَ ٱلْخَٰلِقِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

ٱللَّهَ رَبَّكُمْ وَرَبَّ ءَابَآئِكُمُ ٱلْأَوَّلِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَتَرَكْنَا عَلَيْهِ فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِلْ يَاسِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiAminci ya tabbata ga Ilyãs.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجْزِى ٱلْمُحْسِنِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّهُۥ مِنْ عِبَادِنَا ٱلْمُؤْمِنِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle shĩ, yanã daga bãyin Mu mũminai.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِنَّ لُوطًا لَّمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِذْ نَجَّيْنَٰهُ وَأَهْلَهُۥٓ أَجْمَعِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiA lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِلَّا عَجُوزًا فِى ٱلْغَٰبِرِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

ثُمَّ دَمَّرْنَا ٱلْـَٔاخَرِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِنَّكُمْ لَتَمُرُّونَ عَلَيْهِم مُّصْبِحِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَبِٱلَّيْلِ أَفَلَا تَعْقِلُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِذْ أَبَقَ إِلَى ٱلْفُلْكِ ٱلْمَشْحُونِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiA lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ ٱلْمُدْحَضِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَٱلْتَقَمَهُ ٱلْحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَلَوْلَآ أَنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلْمُسَبِّحِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

لَلَبِثَ فِى بَطْنِهِۦٓ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَنَبَذْنَٰهُ بِٱلْعَرَآءِ وَهُوَ سَقِيمٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَأَنۢبَتْنَا عَلَيْهِ شَجَرَةً مِّن يَقْطِينٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَأَرْسَلْنَٰهُ إِلَىٰ مِا۟ئَةِ أَلْفٍ أَوْ يَزِيدُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَـَٔامَنُوا۟ فَمَتَّعْنَٰهُمْ إِلَىٰ حِينٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَٱسْتَفْتِهِمْ أَلِرَبِّكَ ٱلْبَنَاتُ وَلَهُمُ ٱلْبَنُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَمْ خَلَقْنَا ٱلْمَلَٰٓئِكَةَ إِنَٰثًا وَهُمْ شَٰهِدُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَلَآ إِنَّهُم مِّنْ إِفْكِهِمْ لَيَقُولُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَدَ ٱللَّهُ وَإِنَّهُمْ لَكَٰذِبُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَصْطَفَى ٱلْبَنَاتِ عَلَى ٱلْبَنِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiShin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiMẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannan hukunci)?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَفَلَا تَذَكَّرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiShin, bã ku tunãni?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَمْ لَكُمْ سُلْطَٰنٌ مُّبِينٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKo kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَأْتُوا۟ بِكِتَٰبِكُمْ إِن كُنتُمْ صَٰدِقِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَجَعَلُوا۟ بَيْنَهُۥ وَبَيْنَ ٱلْجِنَّةِ نَسَبًا وَلَقَدْ عَلِمَتِ ٱلْجِنَّةُ إِنَّهُمْ لَمُحْضَرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma suka sanya nasaba a tsakãnin Sa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

سُبْحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَإِنَّكُمْ وَمَا تَعْبُدُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

مَآ أَنتُمْ عَلَيْهِ بِفَٰتِنِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiBa ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِلَّا مَنْ هُوَ صَالِ ٱلْجَحِيمِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَمَا مِنَّآ إِلَّا لَهُۥ مَقَامٌ مَّعْلُومٌ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu,[1] fãce yanã da matsayi sananne."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِنَّا لَنَحْنُ ٱلصَّآفُّونَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِنَّا لَنَحْنُ ٱلْمُسَبِّحُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِن كَانُوا۟ لَيَقُولُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

لَوْ أَنَّ عِندَنَا ذِكْرًا مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

لَكُنَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَكَفَرُوا۟ بِهِۦ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ سَبَقَتْ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا ٱلْمُرْسَلِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle, haƙĩƙa kalmar Mu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّهُمْ لَهُمُ ٱلْمَنصُورُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ ٱلْغَٰلِبُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَأَبْصِرْهُمْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKa nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.[1]

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiShin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمْ فَسَآءَ صَبَاحُ ٱلْمُنذَرِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَتَوَلَّ عَنْهُمْ حَتَّىٰ حِينٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَأَبْصِرْ فَسَوْفَ يُبْصِرُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKa nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

سُبْحَٰنَ رَبِّكَ رَبِّ ٱلْعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَسَلَٰمٌ عَلَى ٱلْمُرْسَلِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma aminci ya tabbata ga Manzanni.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَٱلْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

Kana neman wani jigo? Gwada binciken ma'ana — an bincika tambayarka a cikin ayoyi 6,236.
Harshe — 70