caseriqBinciken ma'ana a cikin Alqur'ani

Suratu Al-Qamar القمر

Ayoyi 55 · Makka · tsarin saukarwa 37

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ ٱقْتَرَبَتِ ٱلسَّاعَةُ وَٱنشَقَّ ٱلْقَمَرُ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSã'a ta yi kusa, kuma wata [1]ya tsãge.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِن يَرَوْا۟ ءَايَةً يُعْرِضُوا۟ وَيَقُولُوا۟ سِحْرٌ مُّسْتَمِرٌّ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma idan sun ga wata ãyã, sai su juya baya su ce: "Sihiri ne mai dõgẽwa!"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَكَذَّبُوا۟ وَٱتَّبَعُوٓا۟ أَهْوَآءَهُمْ وَكُلُّ أَمْرٍ مُّسْتَقِرٌّ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma suka ƙaryata, kuma suka bi son zũciyarsu, alhãli kuwa kõwane al'amari (wanda suke son su tũre daga Annabi) an tabbatar da shi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ جَآءَهُم مِّنَ ٱلْأَنۢبَآءِ مَا فِيهِ مُزْدَجَرٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle, abin da yake akwai tsãwatarwa a cikinsa na lãbãraiya zo musu.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

حِكْمَةٌۢ بَٰلِغَةٌ فَمَا تُغْنِ ٱلنُّذُرُ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiHikima cikakka! Sai dai abũbuwan gargaɗi bã su amfãni.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَتَوَلَّ عَنْهُمْ يَوْمَ يَدْعُ ٱلدَّاعِ إِلَىٰ شَىْءٍ نُّكُرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSabõda haka, ka bar su! Rãnar da mai kiran zai yi kira zuwa ga wani abu abin ƙyama.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

خُشَّعًا أَبْصَٰرُهُمْ يَخْرُجُونَ مِنَ ٱلْأَجْدَاثِ كَأَنَّهُمْ جَرَادٌ مُّنتَشِرٌ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi¡asƙantattu ga idanunsu zã su fito daga kaburburansu, kamar dai sũ fãri ne waɗandasuka wãtse.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

مُّهْطِعِينَ إِلَى ٱلدَّاعِ يَقُولُ ٱلْكَٰفِرُونَ هَٰذَا يَوْمٌ عَسِرٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSunã gaggãwar tafiya zuwa ga mai kiran, kãfirai na cẽwa, "Wannan yini ne mai wuya!"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

كَذَّبَتْ قَبْلَهُمْ قَوْمُ نُوحٍ فَكَذَّبُوا۟ عَبْدَنَا وَقَالُوا۟ مَجْنُونٌ وَٱزْدُجِرَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiMutãnen Nũhu sun ƙaryata, a gabãninsu, sai suka ƙaryata Bawan Mu, kuma suka ce: "Shi mahaukaci ne." Kuma aka tsãwace shi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنِّى مَغْلُوبٌ فَٱنتَصِرْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSabõda haka, ya kira Ubangijinsa (ya ce), "Lalle nĩ, an rinjãye ni, sai Ka yi taimako."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَفَتَحْنَآ أَبْوَٰبَ ٱلسَّمَآءِ بِمَآءٍ مُّنْهَمِرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai Muka bũɗe kõfõfin sama da ruwa mai zuba.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَفَجَّرْنَا ٱلْأَرْضَ عُيُونًا فَٱلْتَقَى ٱلْمَآءُ عَلَىٰٓ أَمْرٍ قَدْ قُدِرَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka ɓuɓɓugar da ƙasã ta zama idãnun ruwa, daɗa ruwa ya haɗu a kan wani umarni da aka riga aka ƙaddara shi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَحَمَلْنَٰهُ عَلَىٰ ذَاتِ أَلْوَٰحٍ وَدُسُرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Muka ɗauke Nũhu a kan (jirgi) na alluna da ƙũsõshi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

تَجْرِى بِأَعْيُنِنَا جَزَآءً لِّمَن كَانَ كُفِرَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTanã gudãna, a kan idãnun Mu, dõmin sakamako ga wanda aka yi wa kãfircin.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَد تَّرَكْنَٰهَآ ءَايَةً فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle, Mun bar ta ta zama ãyã. To, Shin, akwai mai tunãni

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, yãyã azãbã Ta take da gargaɗi Na?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle ne, haƙĩkƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ãni, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

كَذَّبَتْ عَادٌ فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiÃdãwa sun ƙaryata, to, yãya azãbãTa take, da gargaɗi Na?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّآ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ رِيحًا صَرْصَرًا فِى يَوْمِ نَحْسٍ مُّسْتَمِرٍّ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle Mũ, Mun aika da iska mai tsananin sauti a kansu, a cikin wani yinin nahĩsa mai dõgẽwa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

تَنزِعُ ٱلنَّاسَ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ مُّنقَعِرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTanã fizgar mutãne kamar dai sũ kututturan dabĩno tumɓukakku ne.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, yãya azãbã Ta take da gargaɗi Na?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle ne, haƙiƙa Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِٱلنُّذُرِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSamũdãwa sun ƙaryata game da gargaɗin.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَقَالُوٓا۟ أَبَشَرًا مِّنَّا وَٰحِدًا نَّتَّبِعُهُۥٓ إِنَّآ إِذًا لَّفِى ضَلَٰلٍ وَسُعُرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai suka ce: "Wani mutum daga cikinmu, shi kaɗai, wai mu bĩ shi! Lalle mũ a lõkacin, haƙĩƙa mun shiga wata ɓata da haukã.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَءُلْقِىَ ٱلذِّكْرُ عَلَيْهِ مِنۢ بَيْنِنَا بَلْ هُوَ كَذَّابٌ أَشِرٌ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Shin, an jẽfa masa Manzancin ne, a tsakãninmu? Ã'a, shĩ dai gawurtaccen maƙaryaci ne mai girman kai!"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

سَيَعْلَمُونَ غَدًا مَّنِ ٱلْكَذَّابُ ٱلْأَشِرُ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiZã su sani a gõbe, wãne ne gawurtaccen mai ƙaryar, mai girman kan?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّا مُرْسِلُوا۟ ٱلنَّاقَةِ فِتْنَةً لَّهُمْ فَٱرْتَقِبْهُمْ وَٱصْطَبِرْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle Mũ, mãsu aikãwa da rãƙumar[1] ne, ta zame musu fitina, sai ka tsare su da kallo, kuma ka yi haƙuri.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَنَبِّئْهُمْ أَنَّ ٱلْمَآءَ قِسْمَةٌۢ بَيْنَهُمْ كُلُّ شِرْبٍ مُّحْتَضَرٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma ka bã su lãbãri cẽwa ruwa rababbe ne a tsakãninsu (da rãƙumar), kõwane sha, mai shi yanã halartar sa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَنَادَوْا۟ صَاحِبَهُمْ فَتَعَاطَىٰ فَعَقَرَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai suka kira abokinsu, sai ya karɓa, sa'an nan ya sõke ta,

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَكَيْفَ كَانَ عَذَابِى وَنُذُرِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, yãya azãbaTa take da gargaɗi Na?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّآ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ صَيْحَةً وَٰحِدَةً فَكَانُوا۟ كَهَشِيمِ ٱلْمُحْتَظِرِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle Mũ, Mun aika tsãwa guda a kansu, sai suka kasance kamar yãyin mai shinge.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur'ani, dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍۭ بِٱلنُّذُرِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiMutãnen Lũɗu sun ƙaryata, game da gargaɗi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّآ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمْ حَاصِبًا إِلَّآ ءَالَ لُوطٍ نَّجَّيْنَٰهُم بِسَحَرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle Mun aika iskar tsakuwa a kansu, fãce mabiyan Lũɗu, Mun tsirar da su a lõkacin asuba.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

نِّعْمَةً مِّنْ عِندِنَا كَذَٰلِكَ نَجْزِى مَن شَكَرَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSabõda wata ni'ima ta daga gare Mu. Kamar haka Muke sãka wa wanda ya gõde.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ أَنذَرَهُم بَطْشَتَنَا فَتَمَارَوْا۟ بِٱلنُّذُرِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle, haƙĩƙa, ya yi musu gargaɗin damƙar Mu, sai suka yi musu game da gargaɗin.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ رَٰوَدُوهُ عَن ضَيْفِهِۦ فَطَمَسْنَآ أَعْيُنَهُمْ فَذُوقُوا۟ عَذَابِى وَنُذُرِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle haƙĩƙa, su, sun nẽme shi ta wajen bãƙinsa, sai Muka shãfe idãnunsu. "To, ku ɗanɗani azãbaTa da gargaɗĩ Na."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ صَبَّحَهُم بُكْرَةً عَذَابٌ مُّسْتَقِرٌّ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle, haƙĩƙa, wata azãba matabbaciya tã wãye musu gari da yãƙi, tun da sãfe.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَذُوقُوا۟ عَذَابِى وَنُذُرِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, ku ɗanɗani azãbãTa da gargaɗĩ Na.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ يَسَّرْنَا ٱلْقُرْءَانَ لِلذِّكْرِ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun sauƙaƙe Alƙur, ani dõmin tunãwa. To, shin, akwai mai tunãwa?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ جَآءَ ءَالَ فِرْعَوْنَ ٱلنُّذُرُ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle, haƙĩƙa, gargaɗin ya jẽ wa mabiyan Fir'auna.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

كَذَّبُوا۟ بِـَٔايَٰتِنَا كُلِّهَا فَأَخَذْنَٰهُمْ أَخْذَ عَزِيزٍ مُّقْتَدِرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiSun ƙaryata game da ãyõyin Mu, dukansu sai Muka kãma su, irin kãmun Mabuwãyi, Mai ĩkon yi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَكُفَّارُكُمْ خَيْرٌ مِّنْ أُو۟لَٰٓئِكُمْ أَمْ لَكُم بَرَآءَةٌ فِى ٱلزُّبُرِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiShin, kãfiranku ne mafi alhẽri daga waɗancan, ko kuwa kunã da wata barã'a a cikin littattafai?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

أَمْ يَقُولُونَ نَحْنُ جَمِيعٌ مُّنتَصِرٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKõ zã su ce: "Mũ duka mãsu haɗa ƙarfi ne dõmin cin nasara?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

سَيُهْزَمُ ٱلْجَمْعُ وَيُوَلُّونَ ٱلدُّبُرَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiZã a karya[1] tãron, kuma su jũya bãya dõmin gudu.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

بَلِ ٱلسَّاعَةُ مَوْعِدُهُمْ وَٱلسَّاعَةُ أَدْهَىٰ وَأَمَرُّ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiÃ'a, Sã'a ita cẽ lõkacin wa'adinsu, kuma Sã'ar tã fi tsananin masĩfa, kuma ta fiɗãci.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّ ٱلْمُجْرِمِينَ فِى ضَلَٰلٍ وَسُعُرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle ne, mãsu laifi sunã a cikin ɓata da hauka.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

يَوْمَ يُسْحَبُونَ فِى ٱلنَّارِ عَلَىٰ وُجُوهِهِمْ ذُوقُوا۟ مَسَّ سَقَرَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiRãnar da zã a jã su a cikin wuta a kan fuskõkinsu. "Ku ɗanɗani shãfar wutar Saƙar."

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّا كُلَّ شَىْءٍ خَلَقْنَٰهُ بِقَدَرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle Mũ, kõwane irin abu Mun halitta shi a kan tsãri.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَمَآ أَمْرُنَآ إِلَّا وَٰحِدَةٌ كَلَمْحٍۭ بِٱلْبَصَرِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma umurnin Mu bai zamo ba fãce da kalma ɗaya, kamar walƙãwar ido.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ أَهْلَكْنَآ أَشْيَاعَكُمْ فَهَلْ مِن مُّدَّكِرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle ne haƙĩƙa, Mun halaka irin gayyarku. To, shin, akwai mai tunãni?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَكُلُّ شَىْءٍ فَعَلُوهُ فِى ٱلزُّبُرِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma kõwane abu, da suka aikata shi, yanã a cikin littattafai.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَكُلُّ صَغِيرٍ وَكَبِيرٍ مُّسْتَطَرٌ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma dukkan ƙarami da babba, rubutacce ne.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى جَنَّٰتٍ وَنَهَرٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna da kõguna.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فِى مَقْعَدِ صِدْقٍ عِندَ مَلِيكٍ مُّقْتَدِرٍۭ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiA cikin mazaunin gaskiya, wurin Mai ikon yi, Mai iya zartaswa.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

Kana neman wani jigo? Gwada binciken ma'ana — an bincika tambayarka a cikin ayoyi 6,236.
Harshe — 70