Shafin farko › Surori › Suratu Al-Hijr
Suratu Al-Hijr الحجر
Ayoyi 99 · Makka · tsarin saukarwa 54
بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ الٓر تِلْكَ ءَايَٰتُ ٱلْكِتَٰبِ وَقُرْءَانٍ مُّبِينٍ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi A. L̃.R. Waɗan can ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
رُّبَمَا يَوَدُّ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ لَوْ كَانُوا۟ مُسْلِمِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.[1]
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
ذَرْهُمْ يَأْكُلُوا۟ وَيَتَمَتَّعُوا۟ وَيُلْهِهِمُ ٱلْأَمَلُ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa'an nan da sannu zã su sani.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَمَآ أَهْلَكْنَا مِن قَرْيَةٍ إِلَّا وَلَهَا كِتَابٌ مَّعْلُومٌ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
مَّا تَسْبِقُ مِنْ أُمَّةٍ أَجَلَهَا وَمَا يَسْتَـْٔخِرُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَقَالُوا۟ يَٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِى نُزِّلَ عَلَيْهِ ٱلذِّكْرُ إِنَّكَ لَمَجْنُونٌ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
لَّوْ مَا تَأْتِينَا بِٱلْمَلَٰٓئِكَةِ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّٰدِقِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi "Dõmin me bã zã ka zo mana da malã'ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?"
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
مَا نُنَزِّلُ ٱلْمَلَٰٓئِكَةَ إِلَّا بِٱلْحَقِّ وَمَا كَانُوٓا۟ إِذًا مُّنظَرِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Bã Mu sassaukar da malã'iku fãce da gaskiya,[1] bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِنَّا نَحْنُ نَزَّلْنَا ٱلذِّكْرَ وَإِنَّا لَهُۥ لَحَٰفِظُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lale Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا مِن قَبْلِكَ فِى شِيَعِ ٱلْأَوَّلِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãnin ka.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَمَا يَأْتِيهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا كَانُوا۟ بِهِۦ يَسْتَهْزِءُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
كَذَٰلِكَ نَسْلُكُهُۥ فِى قُلُوبِ ٱلْمُجْرِمِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kamar wancan ne Muke shigar da shi[1] a cikin zukãtan mãsu laifi.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
لَا يُؤْمِنُونَ بِهِۦ وَقَدْ خَلَتْ سُنَّةُ ٱلْأَوَّلِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Bã su yin ĩmãni da shi,(4( kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige[1] .
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَلَوْ فَتَحْنَا عَلَيْهِم بَابًا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ فَظَلُّوا۟ فِيهِ يَعْرُجُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
لَقَالُوٓا۟ إِنَّمَا سُكِّرَتْ أَبْصَٰرُنَا بَلْ نَحْنُ قَوْمٌ مَّسْحُورُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã'a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَلَقَدْ جَعَلْنَا فِى ٱلسَّمَآءِ بُرُوجًا وَزَيَّنَّٰهَا لِلنَّٰظِرِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَحَفِظْنَٰهَا مِن كُلِّ شَيْطَٰنٍ رَّجِيمٍ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِلَّا مَنِ ٱسْتَرَقَ ٱلسَّمْعَ فَأَتْبَعَهُۥ شِهَابٌ مُّبِينٌ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَٱلْأَرْضَ مَدَدْنَٰهَا وَأَلْقَيْنَا فِيهَا رَوَٰسِىَ وَأَنۢبَتْنَا فِيهَا مِن كُلِّ شَىْءٍ مَّوْزُونٍ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَجَعَلْنَا لَكُمْ فِيهَا مَعَٰيِشَ وَمَن لَّسْتُمْ لَهُۥ بِرَٰزِقِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã[1] da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَإِن مِّن شَىْءٍ إِلَّا عِندَنَا خَزَآئِنُهُۥ وَمَا نُنَزِّلُهُۥٓ إِلَّا بِقَدَرٍ مَّعْلُومٍ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَأَرْسَلْنَا ٱلرِّيَٰحَ لَوَٰقِحَ فَأَنزَلْنَا مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءً فَأَسْقَيْنَٰكُمُوهُ وَمَآ أَنتُمْ لَهُۥ بِخَٰزِنِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَإِنَّا لَنَحْنُ نُحْىِۦ وَنُمِيتُ وَنَحْنُ ٱلْوَٰرِثُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَلَقَدْ عَلِمْنَا ٱلْمُسْتَقْدِمِينَ مِنكُمْ وَلَقَدْ عَلِمْنَا ٱلْمُسْتَـْٔخِرِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَإِنَّ رَبَّكَ هُوَ يَحْشُرُهُمْ إِنَّهُۥ حَكِيمٌ عَلِيمٌ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَلَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَٰنَ مِن صَلْصَٰلٍ مِّنْ حَمَإٍ مَّسْنُونٍ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَٱلْجَآنَّ خَلَقْنَٰهُ مِن قَبْلُ مِن نَّارِ ٱلسَّمُومِ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar[1] iskar zafi.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَإِذْ قَالَ رَبُّكَ لِلْمَلَٰٓئِكَةِ إِنِّى خَٰلِقٌۢ بَشَرًا مِّن صَلْصَٰلٍ مِّنْ حَمَإٍ مَّسْنُونٍ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã'iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَإِذَا سَوَّيْتُهُۥ وَنَفَخْتُ فِيهِ مِن رُّوحِى فَقَعُوا۟ لَهُۥ سَٰجِدِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi "To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa[1] a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَسَجَدَ ٱلْمَلَٰٓئِكَةُ كُلُّهُمْ أَجْمَعُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِلَّآ إِبْلِيسَ أَبَىٰٓ أَن يَكُونَ مَعَ ٱلسَّٰجِدِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancẽwa daga mãsu yin sujadar.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالَ يَٰٓإِبْلِيسُ مَا لَكَ أَلَّا تَكُونَ مَعَ ٱلسَّٰجِدِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ya ce: "Yã Iblĩs mẽne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba?"
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالَ لَمْ أَكُن لِّأَسْجُدَ لِبَشَرٍ خَلَقْتَهُۥ مِن صَلْصَٰلٍ مِّنْ حَمَإٍ مَّسْنُونٍ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالَ فَٱخْرُجْ مِنْهَا فَإِنَّكَ رَجِيمٌ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَإِنَّ عَلَيْكَ ٱللَّعْنَةَ إِلَىٰ يَوْمِ ٱلدِّينِ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi "Kuma lalle ne akwai la'ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالَ رَبِّ فَأَنظِرْنِىٓ إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالَ فَإِنَّكَ مِنَ ٱلْمُنظَرِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِلَىٰ يَوْمِ ٱلْوَقْتِ ٱلْمَعْلُومِ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi "Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sanan ne."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالَ رَبِّ بِمَآ أَغْوَيْتَنِى لَأُزَيِّنَنَّ لَهُمْ فِى ٱلْأَرْضِ وَلَأُغْوِيَنَّهُمْ أَجْمَعِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِلَّا عِبَادَكَ مِنْهُمُ ٱلْمُخْلَصِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi "Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالَ هَٰذَا صِرَٰطٌ عَلَىَّ مُسْتَقِيمٌ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِنَّ عِبَادِى لَيْسَ لَكَ عَلَيْهِمْ سُلْطَٰنٌ إِلَّا مَنِ ٱتَّبَعَكَ مِنَ ٱلْغَاوِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi "Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَإِنَّ جَهَنَّمَ لَمَوْعِدُهُمْ أَجْمَعِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma'akawartarsu gabã ɗaya.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
لَهَا سَبْعَةُ أَبْوَٰبٍ لِّكُلِّ بَابٍ مِّنْهُمْ جُزْءٌ مَّقْسُومٌ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Tanã da ƙõfõfi bakwai,[1] ga kõwace ƙõfa akwai wani juz'i daga gare su rababbe.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى جَنَّٰتٍ وَعُيُونٍ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
ٱدْخُلُوهَا بِسَلَٰمٍ ءَامِنِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi "Ku shigẽ ta da aminci, kunã amintattu."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَنَزَعْنَا مَا فِى صُدُورِهِم مِّنْ غِلٍّ إِخْوَٰنًا عَلَىٰ سُرُرٍ مُّتَقَٰبِلِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma Muka ɗẽbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama 'yan'uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
لَا يَمَسُّهُمْ فِيهَا نَصَبٌ وَمَا هُم مِّنْهَا بِمُخْرَجِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga, cikin ta ba.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
نَبِّئْ عِبَادِىٓ أَنِّىٓ أَنَا ٱلْغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ka bai wa bãyiNa lãbari cẽwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَأَنَّ عَذَابِى هُوَ ٱلْعَذَابُ ٱلْأَلِيمُ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma azãbãTa ita ce Azãba mai raɗaɗi.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَنَبِّئْهُمْ عَن ضَيْفِ إِبْرَٰهِيمَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِذْ دَخَلُوا۟ عَلَيْهِ فَقَالُوا۟ سَلَٰمًا قَالَ إِنَّا مِنكُمْ وَجِلُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالُوا۟ لَا تَوْجَلْ إِنَّا نُبَشِّرُكَ بِغُلَٰمٍ عَلِيمٍ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi makabushãra game da wani yãro masani."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالَ أَبَشَّرْتُمُونِى عَلَىٰٓ أَن مَّسَّنِىَ ٱلْكِبَرُ فَبِمَ تُبَشِّرُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra[1] ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara?"
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالُوا۟ بَشَّرْنَٰكَ بِٱلْحَقِّ فَلَا تَكُن مِّنَ ٱلْقَٰنِطِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالَ وَمَن يَقْنَطُ مِن رَّحْمَةِ رَبِّهِۦٓ إِلَّا ٱلضَّآلُّونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijin sa, fãce ɓatattu?"
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالَ فَمَا خَطْبُكُمْ أَيُّهَا ٱلْمُرْسَلُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ya ce: "To, mẽne ne babban al'amarinku? Yã kũ manzanni!"
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالُوٓا۟ إِنَّآ أُرْسِلْنَآ إِلَىٰ قَوْمٍ مُّجْرِمِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِلَّآ ءَالَ لُوطٍ إِنَّا لَمُنَجُّوهُمْ أَجْمَعِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi "Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِلَّا ٱمْرَأَتَهُۥ قَدَّرْنَآ إِنَّهَا لَمِنَ ٱلْغَٰبِرِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi "Fãce mãtarsa mun ƙaddara cẽwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَلَمَّا جَآءَ ءَالَ لُوطٍ ٱلْمُرْسَلُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi To, a lõkacin da mazannin suka jẽ wa mutãnen Lũɗu,
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالَ إِنَّكُمْ قَوْمٌ مُّنكَرُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالُوا۟ بَلْ جِئْنَٰكَ بِمَا كَانُوا۟ فِيهِ يَمْتَرُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Suka ce: "Ã'a, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَأَتَيْنَٰكَ بِٱلْحَقِّ وَإِنَّا لَصَٰدِقُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi "Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَأَسْرِ بِأَهْلِكَ بِقِطْعٍ مِّنَ ٱلَّيْلِ وَٱتَّبِعْ أَدْبَٰرَهُمْ وَلَا يَلْتَفِتْ مِنكُمْ أَحَدٌ وَٱمْضُوا۟ حَيْثُ تُؤْمَرُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi "Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka aumurce ku."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَقَضَيْنَآ إِلَيْهِ ذَٰلِكَ ٱلْأَمْرَ أَنَّ دَابِرَ هَٰٓؤُلَآءِ مَقْطُوعٌ مُّصْبِحِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma Muka hukunta wancan al'amarin zuwa gare shi cẽwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankẽwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga Asuba.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَجَآءَ أَهْلُ ٱلْمَدِينَةِ يَسْتَبْشِرُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالَ إِنَّ هَٰٓؤُلَآءِ ضَيْفِى فَلَا تَفْضَحُونِ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَلَا تُخْزُونِ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi "Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالُوٓا۟ أَوَلَمْ نَنْهَكَ عَنِ ٱلْعَٰلَمِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba?"
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالَ هَٰٓؤُلَآءِ بَنَاتِىٓ إِن كُنتُمْ فَٰعِلِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Ya ce: "Ga waɗannan, 'ya'yãna[1] idan kun kasance mãsu aikatãwa ne."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
لَعَمْرُكَ إِنَّهُمْ لَفِى سَكْرَتِهِمْ يَعْمَهُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Rantsuwa da[1] rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَأَخَذَتْهُمُ ٱلصَّيْحَةُ مُشْرِقِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Sa'an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَجَعَلْنَا عَٰلِيَهَا سَافِلَهَا وَأَمْطَرْنَا عَلَيْهِمْ حِجَارَةً مِّن سِجِّيلٍ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Sa'an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَٰتٍ لِّلْمُتَوَسِّمِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَإِنَّهَا لَبِسَبِيلٍ مُّقِيمٍ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a gẽfen wata hanyã tabbatacciya.[1]
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةً لِّلْمُؤْمِنِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَإِن كَانَ أَصْحَٰبُ ٱلْأَيْكَةِ لَظَٰلِمِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma lalle ne ma'abũta Al'aika[1] sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci!
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَٱنتَقَمْنَا مِنْهُمْ وَإِنَّهُمَا لَبِإِمَامٍ مُّبِينٍ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a gẽfen wani tafarki mabayyani.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَلَقَدْ كَذَّبَ أَصْحَٰبُ ٱلْحِجْرِ ٱلْمُرْسَلِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma lalle ne haƙĩƙa ma'abũta Hijiri[1] sun ƙaryata Manzanni.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَءَاتَيْنَٰهُمْ ءَايَٰتِنَا فَكَانُوا۟ عَنْهَا مُعْرِضِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma Kuka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirẽwa daga gare su.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَكَانُوا۟ يَنْحِتُونَ مِنَ ٱلْجِبَالِ بُيُوتًا ءَامِنِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَأَخَذَتْهُمُ ٱلصَّيْحَةُ مُصْبِحِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga Asuba.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَمَآ أَغْنَىٰ عَنْهُم مَّا كَانُوا۟ يَكْسِبُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Sa'an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَمَا خَلَقْنَا ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضَ وَمَا بَيْنَهُمَآ إِلَّا بِٱلْحَقِّ وَإِنَّ ٱلسَّاعَةَ لَـَٔاتِيَةٌ فَٱصْفَحِ ٱلصَّفْحَ ٱلْجَمِيلَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã'a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِنَّ رَبَّكَ هُوَ ٱلْخَلَّٰقُ ٱلْعَلِيمُ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَلَقَدْ ءَاتَيْنَٰكَ سَبْعًا مِّنَ ٱلْمَثَانِى وَٱلْقُرْءَانَ ٱلْعَظِيمَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗan da ake maimaita karatunsu[1] da Alƙur'ãni mai girma.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
لَا تَمُدَّنَّ عَيْنَيْكَ إِلَىٰ مَا مَتَّعْنَا بِهِۦٓ أَزْوَٰجًا مِّنْهُمْ وَلَا تَحْزَنْ عَلَيْهِمْ وَٱخْفِضْ جَنَاحَكَ لِلْمُؤْمِنِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau'i-nau'i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَقُلْ إِنِّىٓ أَنَا ٱلنَّذِيرُ ٱلْمُبِينُ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyanan ne."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
كَمَآ أَنزَلْنَا عَلَى ٱلْمُقْتَسِمِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa,[1]
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
ٱلَّذِينَ جَعَلُوا۟ ٱلْقُرْءَانَ عِضِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Waɗanda suka sanya Alƙur'ãni tãtsuniyõyi.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَوَرَبِّكَ لَنَسْـَٔلَنَّهُمْ أَجْمَعِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi To, rantsuwa da Ubangijinka![1] Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
عَمَّا كَانُوا۟ يَعْمَلُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَٱصْدَعْ بِمَا تُؤْمَرُ وَأَعْرِضْ عَنِ ٱلْمُشْرِكِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِنَّا كَفَيْنَٰكَ ٱلْمُسْتَهْزِءِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu[1] izgili.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
ٱلَّذِينَ يَجْعَلُونَ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa'an nan da sannu zã su sani.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَلَقَدْ نَعْلَمُ أَنَّكَ يَضِيقُ صَدْرُكَ بِمَا يَقُولُونَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cẽwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili).
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ وَكُن مِّنَ ٱلسَّٰجِدِينَ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَٱعْبُدْ رَبَّكَ حَتَّىٰ يَأْتِيَكَ ٱلْيَقِينُ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
← Suratu Ibrahim
Suratu An-Nahl →
Kana neman wani jigo? Gwada binciken ma'ana — an bincika tambayarka a cikin ayoyi 6,236.
→
Rubutun Larabci da fassarori ta Tanzil da QuranEnc — kalma-da-kalma, ba a canza ba · Fassarori mallakar masu fassara ne kuma ba Alqur'ani kansa ba
Wannan kayan aikin bincike ne, ba tushen fatawa ba.