Suratu An-Naazi'aat النازعات
Ayoyi 46 · Makka · tsarin saukarwa 81
بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ وَٱلنَّٰزِعَٰتِ غَرْقًا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiIna rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَٱلنَّٰشِطَٰتِ نَشْطًا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiDa mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَٱلسَّٰبِحَٰتِ سَبْحًا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiDa mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَٱلسَّٰبِقَٰتِ سَبْقًا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiSa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umarnin Allah) kamar suna tsẽre.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَٱلْمُدَبِّرَٰتِ أَمْرًا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiSa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umarni.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
يَوْمَ تَرْجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiRãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
تَتْبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiMai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiWasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
أَبْصَٰرُهَا خَٰشِعَةٌ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiAlhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِى ٱلْحَافِرَةِ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiSunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
أَءِذَا كُنَّا عِظَٰمًا نَّخِرَةً
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
قَالُوا۟ تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiSuka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌ وَٰحِدَةٌ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai kawai gã su a bãyan ƙasa.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiShin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى
Hausa Translation - Abu Bakr JumiA lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiKa tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoron Sa?"
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَأَرَىٰهُ ٱلْـَٔايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai ya nũna masa ãyar[1] nan mafi girma.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiSa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiSai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْـَٔاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiSabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةً لِّمَن يَخْشَىٰٓ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
ءَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُ بَنَىٰهَا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiShin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّىٰهَا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiYa ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَىٰهَا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَٱلْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
أَخْرَجَ مِنْهَا مَآءَهَا وَمَرْعَىٰهَا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiYa fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَٱلْجِبَالَ أَرْسَىٰهَا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiDa duwatsu, Yã kafe ta.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
مَتَٰعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَٰمِكُمْ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiDomin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلْكُبْرَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
يَوْمَ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَٰنُ مَا سَعَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiRãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَأَمَّا مَن طَغَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, amma wanda ya yi girman kai.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَءَاثَرَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَإِنَّ ٱلْجَحِيمَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفْسَ عَنِ ٱلْهَوَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فَإِنَّ ٱلْجَنَّةَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
يَسْـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَىٰهَا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiSunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَىٰهَآ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiMe ya haɗã ka da ambatonta?
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ
Hausa Translation - Abu Bakr JumiZuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَىٰهَا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiKai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوٓا۟ إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَىٰهَا
Hausa Translation - Abu Bakr JumiKamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.
Duba dukkan fassarorin wannan aya →
Kana neman wani jigo? Gwada binciken ma'ana — an bincika tambayarka a cikin ayoyi 6,236.
→