caseriqBinciken ma'ana a cikin Alqur'ani

Suratu At-Takwir التكوير

Ayoyi 29 · Makka · tsarin saukarwa 7

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ إِذَا ٱلشَّمْسُ كُوِّرَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiIdan rãna aka shafe haskenta

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِذَا ٱلْجِبَالُ سُيِّرَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِذَا ٱلْعِشَارُ عُطِّلَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma idan rãƙuma mãsu cikunna[1] aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِذَا ٱلْوُحُوشُ حُشِرَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِذَا ٱلْبِحَارُ سُجِّرَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma idan rãyuka aka haɗa[1] su da jikunkunansu.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِذَا ٱلْمَوْءُۥدَةُ سُئِلَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma idan wadda aka turbuɗe[1] ta da rai aka tambaye ta.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

بِأَىِّ ذَنۢبٍ قُتِلَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr Jumi"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiIdan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma idan sama aka fẽɗe ta.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِذَا ٱلْجَحِيمُ سُعِّرَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma idan Jahĩm aka hũra ta

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَإِذَا ٱلْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma idan Aljanna aka kusantar da ita.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّآ أَحْضَرَتْ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiRai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلْخُنَّسِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiTo, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã[1] ba.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

ٱلْجَوَارِ ٱلْكُنَّسِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiMãsu gudu suna ɓũya.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَٱلَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiDa dare idan ya bãyar da bãya.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَٱلصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiDa sãfiya idan ta yi lumfashi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

ذِى قُوَّةٍ عِندَ ذِى ٱلْعَرْشِ مَكِينٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiMai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

مُّطَاعٍ ثَمَّ أَمِينٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiWanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma abokinku ba mahaukaci ba ne.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَلَقَدْ رَءَاهُ بِٱلْأُفُقِ ٱلْمُبِينِ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma lalle ne, yã gan shi[1] a cikin sararin sama mabayyani.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَمَا هُوَ عَلَى ٱلْغَيْبِ بِضَنِينٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma shi, ga gaibi[1] bã mai rowa ba ne.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَٰنٍ رَّجِيمٍ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiShin, a inã zã ku tafi?

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَٰلَمِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiLalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiGa wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلْعَٰلَمِينَ

Hausa Translation - Abu Bakr JumiKuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.

Duba dukkan fassarorin wannan aya →

Kana neman wani jigo? Gwada binciken ma'ana — an bincika tambayarka a cikin ayoyi 6,236.
Harshe — 70